'Yar takarar gomna wacce ta akiye mukaminta na minista Hajiya Aisha Jummai Alhassan ta bayyana dalilinda yasa ta fice daga jamiyyar APC.
Hajiya Aisha aika da wasikar barin aiki ga fadar shugaban kasa bayan ta fice daga jam'iyyar APC sakamakon kin tantanceta cikin jerin wadanda zasuyi takarar gomna a zaben fidda gwani da za'a gudanar.
"Na zabi komawa jam'iyyar UDP saboda soyayya karamar jam'iyya ce mai manufofi masu kyau. Sannan ina ganin hakan shine daidai a demokradiyya, yanzu fa talakawa sun waye babu ruwansu da wace jam'iyya kake halin mutum jarinsa.
Idan baku manta ba a kwanakin baya ne Hajia Aisha Jummai ta nuna goyon bayanta ga tshohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar wanda shine ubangidanta a siyasa. Yana cikin dalilai da suka hassala shugabannin APC hartakai ga kin tantanceta.
Aisha Jummai Alhassan tshohuwar Senata ce wacce tayi tajarat
Ajiye aikin Maman Taraba ya jawo cece kuce musamman a kafafen sadarwa inda wasu ke ganin tayi daidai wasu magoya bayan APC kuma ke cewa "ALLAH RAKA TAKI GONA".

